in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babu bukatar tattauna bukatun da kasashe hudu suka gabatarwa Qatar, in ji Saudiya
2017-06-28 10:38:23 cri
Ministan harkokin wajen kasar Saudiya Adel al-Jubeir ya bayyana a jiya Talata cewa, ya kamata kasar Qatar ta warware matsalar katse huldar jakadanci da take fuskanta da kasashen nan hudu.

Mr. Jubeir ya ce, kasashen hudu da suka hada da Saudiya, da Masar, da Hadaddiyar daular Larabawa da kuma Bahrain, ba za su yi shawarwari da kasar Qatar kan bukatun da suka gabatar mata ba.

Haka kuma, bisa labarin da aka samu, an ce, ministan harkokin wajen kasar Qatar Mohammed bin Abdulrahman Al-Thani zai kai ziyarar aiki a kasar Amurka, domin tattaunawa da bangaren Amurka, kan matsalar katse huldar jakadanci da kasar sa ke fama da ita a halin yanzu.

A ranar 5 ga watan nan ne, kasashen hudu suka katse huldar jakadanci dake tsakaninsu da kasar Qatar bisa zargin cewa, kasar Qatar tana goyon bayan 'yan ta'adda, wadanda ke haifar da barazana ga yanayin tsaron yankin, sa'an nan, kasashen hudu sun fara hana jigilar kayayyaki a tsakaninsu da kasar Qatar.

Daga bisani kuma, wasu kasashe sun sanar da katse huldar jakadanci dake tsakaninsu da kasar Qatar.

Bisa labarin da aka fidda a ranar 23 ga wata, an ce, kasashe hudu sun riga sun gabatar da bukatu guda 13 ga kasar Qatar, domin warware matsalar katse huldar jakadancin da ita, inda suka kuma bukaci kasar Qatar da ta amince da bukatunsu cikin kwanaki 10. To sai dai kuma Qatar din ta bayyana cewa, bukatun da kasashen hudu suka gabatar mata, sun sabawa 'yancin mulkin kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China