in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan, Masar da Habasha sun kulla yarjejeniyar nazarin shirin gina madatsar ruwa ta Renaissance
2016-09-21 11:19:57 cri
Tawagogin ayyukan ban ruwa na kasashen Sudan, Masar da Habasha sun kulla wata yarjejeniyar nazarin shirin gina madatsar ruwa ta Renaissance a babban birnin kasar Sudan, Khartoum, domin sa ido da kuma yin bincike kan tasirin da kafuwar madatsar ruwan na Renaissance za ta yi wa wasu kasashen da abin ya shafa, ta yadda za su iya warware matsalolin da mai iyu za a gamu da su cikin lokaci.

A shekarar 2013, gwamnatin kasar Habasha ta sanar da gina madatsar ruwa ta Renaissance dake kan kogin Blue Nile dake yankin iyaka a tsakanin Habasha da Sudan, domin kara samar da wutar lantarki a kasar da dai sauransu, amma, kasar Masar ta ki yarda da shirin din da gwamnatin Habasha ta fid da, sabo da tana damuwar cewa, idan madatsar ruwan na Renaissance ta kafu, yawan ruwa a karshen kogin Nile zai ragu sosai, lamarin da zai haddasa babbar illa ga tattalin arzikin kasar Masar.

Sabo da haka, kasashen Sudan, Masar da Habasha sun yi shawarwari kan wannan batu sau da dama, amma ba tare da cimma matsaya daya ba. Sa'an nan, cikin shekarar 2015 da ta wuce, wadannan kasashe uku sun kulla wata sanarwar ka'idoji, inda suka amince da gina madatsar ruwa ta Renaissance, a sa'i daya kuma, gwamnatocin kasashen uku sun bukaci a yi nazari kan tasirin da wannan aiki zai haifar wa kasashen da abin ya shafa, domin tabbatar da samun isassun ruwa a kasashensu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China