in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD za ta taimaka wajen magance rikicin kabilanci a kan iyakar Kenya da Habasha
2016-08-09 10:47:48 cri
MDD ta ce za ta bullo da wani shiri na musamman da nufin dakile yawaitar rikice-rikicen kabilanci a kan iyakar kasashen Kenya da Habasha.

Mai rikon mukamin jami'in MDD a Kenya Siddarth Chatterjee, ya fadawa kamfanin dillancin labarun kasar Sin Xinhua a Nairobi cewa, tuni kasar Amurka ta kashe kudi kimanin dala miliyan 7 domin aikin wanzar da zaman lafiya a Kenya.

Chatterjee ya ce, MDD ta ware makudan kudade domin amfani da su wajen rage yawaitar rikicin kabilanci daga bangaren kasar Habasha.

Chatterjee ya fada a lokacin taro game da cigaban kasashen shiyyar gabashin Afrika da magance rikice-rikice da tsattsauran ra'ayi cewar, MDD a shirye take ta zuba kudade domin inganta fannonin cigaban rayuwar al'umma musamman samar da ilmi da kiwon lafiya.

Shirin kiyaye zaman lafiyar na hadin gwiwa ne tsakanin MDD da hukumar cigaban kasashen gabashin Afrika IGAD, da kuma kasashen Kenya da Habasha.

Chatterjee ya ce, ana sa ran samun cikakken zaman lafiya da kwanciyar hankali nan da shekaru 5 masu zuwa, kasancewar shugabannin kasashen da abin ya shafa suna daukar matakan da suka dace don warware rikicin ta hanyar siyasa.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China