in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar kiwon lafiyar Sudan ta yi musu kan barkewar kwalara a kasar
2016-09-17 13:25:04 cri
Jiya Jumma'a 16 ga wata, hukumar kiwon lafiya ta kasar Sudan ta fidda wata sanarwa, inda ta ce, yanzu, an riga an hana yaduwar wata cutar zawayi dake haddasa rasuwar mutane a yankin kudu maso gabashin kasar yadda ya kamata, shi ya sa, babu bukata da hukumar kiwon lafiyar duniya watau WHO ta sa hannu kan lamarin a kasar. Sa'an nan, cikin sanarwar din da Sudan ta bayar, ta yi musu kan labarin yaduwar kwalara da kuma rasuwar wadannan mutane.

Kafin haka kuma, wasu kafofin watsa labarai sun ba da labarin cewa, cutar zawayi ta riga ta haddasa rasuwar mutane kimanin dari daya a jihar Blue Nile, kuma galibi daga cikinsu yara ne, mazaunan wurin suna kuma bayyana damuwar cewa, cutar kwalara ce ta haddasa amai da gudana ga mutanen. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China