in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta samar wa Uganda taimakon jin kai na gaggawa
2016-01-31 13:27:19 cri
Ofishin kula da 'yan gudun hijira na MDD ya fidda rahoto a ran 29 ga wata cewa, ya riga ya samar wa kasar Uganda dallar Amurka miliyan 18 domin ba ta taimakon jin kai na gaggawa, watau taimaka wa 'yan gudun hijira kimanin dubu 510 da suka shiga kasar daga kasashen kewayenta.

MDD ta riga ta shigar da kasar Uganda cikin jerin kasashe guda tara dake bukatar taimakon jin kai na gaggawa, kuma za a yi amfani da taimakon kudin wajen bai wa 'yan gudun hijira dake kasar Uganda kayayyakin zaman rayuwa na yau da kullum, domin biyan bukatunsu na gaggawa.

Ana samun yanayin siyasa na zama karko a kasar Uganda, a halin yanzu, 'yan gudun hijira sama da dubu dari biyar suna zama a wannan kasar, kuma galibi daga cikinsu sun zo daga kasashen Congo(Kinshasa), Sudan ta Kudu, Burundi da kuma Somaliya.

Kaza lika, bisa kididdigar da aka yi, 'yan gudun hijira sama da dubu 110 suka shiga kasar Uganda a shekarar 2015, lamarin da ya sa, kasar ta kasance a matsayi na uku cikin manyan kasashen Afirka wadanda suka fi karbar 'yan gudun hijira, yayin da take a matsayi na takwas cikin kasashen duniya kan wannan batu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China