in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Uganda ya yaba ma kasar Sin yadda ba ta tsoma baki a cikin harkokin wassu kasashe ba
2015-10-03 13:04:53 cri
Shugaban kasar Uganda, Yuweri Musaveni ya yaba ma kasar Sin yadda ba ta tsoma baki a cikin harkokin wassu kasashe. Yana mai cewa kasashe ba sa bukatar a koya musu yadda za su tafiyar da al'amurransu.

Shugaba Musaveni ya bayyana hakan ne a wajen liyafar murnar cika shekaru 66 da kafa sabuwar kasar Sin da aka yi a ofishin jakadancin Sin dake Kamfala, babban birnin kasar Uganda.

A cikin jawabinsa ya ce kasar Sin tana yin taka tsantsan wajen tsoma baki a harkokin kasashe kuma tana nacewa ga bin ka'idojin MDD na daina yin hakan wanda jawabin shi ke misali da tsoma bakin kasashen yammaci da suke nuna ikonsu a kan kasashen Afrika kan yadda za su tafiyar da mulkinsu.

A nashi jawabin Jakadan kasar Sin a Uganda Zhao Yali ya ce kasar Sa za ta ci gaba da tabbaar da samar da zaman lafiya a duniya kuma komai runtsin da za'a shiga ba za ta rabu ko ta nemi mamaye wadansu ba.

Bikin ya samu halartar manyan jami'an gwamnatin kasar ta Uganda da sauran Jami'an diplomasiya na kasashen dake kasar Uganda. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China