in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Angela Merkel ta yi kira da a yanke wa 'yan gudun hijirar da suka aikata laifufuka hukunci mai tsanani
2016-01-10 14:16:16 cri
Shugabar gwamnatin Jamus, Angela Merkel ta nuna goyon baya kawo gyara wasu ayoyin doka a ran 9 ga wata, don neman yanke hunkuci mai tsanani ga 'yan gudun hijira da wadanda suke neman mafaka da suka aikata laifufuka a kasar.

Jam'iyyar CDU dake karkashin jagorancin Merkel ta kira wani taron koli a wannan rana, don tattauna kan laifin cin zarafin mata da sace-sace da suka faru a birnin Cologne dake yammacin kasar Jamus. Ya zuwa yanzu, al'amarin da ya faru a Cologne ya kara tsananta. Masu kyamar 'yan kasashen waje sun yi zanga-zanga a ran 9 ga wata a Cologne saboda ganin aukuwar al'amarin, zanga-zangat da suka yi ta haifar da rikici, abin da ya sa 'yan sandan wurin suka tarwatsa masu zanga-zanga da bindigar ruwa mai karfi tare kuma da cafke wasu daga cikinsu.

Taron koli kuma ya ba da sanarwar yin kira da a saukaka dokoki kan korar bakin da suka aikata laifi a kasar, idan wani dan gudun hijira ko wanda ya nemi samun mafaka sun aikata laifi kuma an yanke masa hukunci, ba zai sami iznin zama a Jamus ba, kuma za a kore shi. Bisa tanade-tanaden dokokin na yanzu a kasar ta Jamus, ba za a kori wanda yake neman mafaka daga kasar ba, sai dai idan ya aikata laifi da aka yanke masa hukunci da daurin shekaru 3 ko fiye a gidan kurkuku. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China