in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kawancin jam'iyyun CDU/SCU ta kasar Jamus ta samu gagarumar nasara a babban zaben kasar
2013-09-24 16:51:14 cri
Rahotanni sun bayyana kammala zaben majalisar dokokin kasar Jamus a ran 22 ga wata cikin kyakkyawan yanayi, inda shugabar gwamnatin kasar Angela Merkel, da kawancen jam'iyyun CDU/CSU dake karkashin shugabancinta ya cimma gagarumar nasara, matakin da mai yiwuwa ne ya baiwa kawacen damar gudanar da mulkin kasar kai tsaye. Kuma kasashen duniya sun taya Merkel, da jam'iyyarta murna kan wannan nasarar da suka cimma.

Firaminitan kasar Sin Li Keqiang ya zanta da Merkel ta wayar tarho a daren ranar Litinin 23 ga wata, domin taya ta murna, inda ya nuna cewa, gwamnatin kasar Sin tana fatan kara habaka zumunci tsakaninta da Jamus. A nata bangare, Madam Merkel ta furta cewa, Jamus na fatan kara zurfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma kara habaka hadin kai a fannonin daban-daban.

Shugaban majalisar gudanarwa ta kungiyar kawancen kasashen Turai Mr Von Rompuy, da shugaban kasar Faransa Francois Hollande, su ma sun taya Merkel murnar lashe zaben. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China