in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jamus tana shirin samar da goyon baya a fannin aikin soja ga kasar Faransa don yaki da ta'addanci
2015-11-27 11:05:48 cri
Bisa labarin da kafofin watsa labaru na kasar Jamus suka bayar a ranar 26 ga wata, an ce, gwamnatin kasar Jamus tana shirin baiwa kasar Faransa goyon baya a fannin aikin soja don yaki da kungiyar IS a kasar Syria.

Kamfanin dillancin labaru na DPA na kasar Jamus ya ruwaito jami'in gwamnatin kasar na cewa, shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel da ministocin da abin ya shafa sun tsaida wannnan kuduri ne a taron da aka gudanar a birnin Berlin a wannan rana. An bayyana cewa, gwamnatin kasar Jamus tana shirin tura jiragen saman bincike, wani jirgin ruwan yaki, jirgin saman samar da mai a yayin da jiragen yakin ke tafiya a sama a kalla daya, da kuma yin bincike ta tauraron dan Adam don nuna goyon baya ga Faransa.

A jiya shugaban kasar Faransa François Hollande ya bayyana bayan da ya gana da shugaba Merkel a birnin Paris cewa, Faransa da Jamus za su hada kai don yaki da ta'addanci tare. Ministan harkokin tsaron kasar Jamus Ursula von der Leyen ya bayyana a jiya cewa, Jamus za ta kara tura sojoji zuwa kasar Mali don taimakawa kasar Faransa a kokarin da ta ke na tabbatar da zaman lafiya a kasar Mali, hakan zai rage matsin lamba da kasar Faransa ke fuskanta a yakin da ta ke yi da kungiyar IS. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China