in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Zuma ya jinjinawa kwazon kasar Sin game da tallafawa wanzar da zaman lafiya
2015-09-05 13:03:44 cri
Shugaba Jacob Zuma na Afirka ta Kudu, ya jinjinawa kwazon kasar Sin a fannin goyon bayan manufofin wanzar da zaman lafiya a duniya baki daya. Zuma ya bayyana hakan ne a ranar Jumma'a, bayan kammala kallon faretin soji da kasar Sin ta gudanar a ranar Alhamis a nan birnin Beijing.

Ya ce hakika faretin ya kayatar, ya kuma bayyana karfin kasar ta Sin a fannin aikin soji, da kuma niyyarta ta ci gaba da amfani da ikon da take da shi wajen wanzar da tsaro, da zaman lafiya da lumana a duniya baki daya.

Zuma ya ce kasarsa, ta yi matukar farin cikin gayyatar da ta samu na halartar wannan biki na bana, musamman kasancewar Sin kasar dake goyon bayan manufar kyamar nuna karfin tuwo, da tsaron yankunanta, da kuma bunkasa manufar watsi da amfani da karfi a duniya baki daya.

Bugu da kari shugaban na Afirka ta Kudu, ya jaddada muhimmnacin rawar da Sin ta taka wajen goyon bayan manufar samun 'yancin kan kasashen Afirka. Hakan a cewarsa ya dada fitowa fili, idan aka dubi yadda kasashen na Afirka 9 suka halarci bikin na bana.

Daga nan sai ya bayyana muhimmnacin koyi daga Sin, yana mai cewa kishin kasa da da'a, na cikin muhimman darussa da nahiyar Afirka ka iya koya daga Sin. Ya kuma yi fatan ganin kasarsa ta karfafa ikonta a fannin tsaro, ta yadda hakan zai zamo daya daga cikin matakai na wanzar da tsaro, da zaman lafiya a nahiyar Afirka baki daya. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China