in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a habaka hadin gwiwa a manyan fannoni biyar a gun taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afrika
2015-10-10 18:14:44 cri
Mamba a majalisar gudanarwa ta kasar Sin Mista Yang Jiechi ya yi jawabi lokacin da yake ziyarar aiki a kasar Afrika ta kudu a ranar asabar din nan cewa, Sin da Afrika za su yi amfani da zarafi mai kyau saboda ganin taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu da za a yi a karshen wannan shekara a kasar Afrika ta kudu,don kara hadin gwiwa tsakaninsu a wasu manyan fannoni, ciki hadda bunkasa masana'antu, sha'anin noma na zamani, kiwon lafiya, musayar al'adu, da shimfidar zaman lafiya da tabbatar da tsaro.

Mista Yang ya bayyana cewa, ziyararsa a wannan karo na da zummar yin musayar ra'ayi kan yadda za a shirya wannan taro da za a yi a watan Disamba na bana a birnin Johannesburg na kasar Afrika ta kudu. A cewarsa, tun kafuwar wannan dandali na tsawon shekaru 15 da suka gabata, bangarorin biyu na samun ci gaba mai armashi a fannoni daban-daban cikin hadin gwiwa.

Ban da wannan kuma, Mista Yang ya ce, yanzu dandalin ya zama wani tsari mai inganci wajen yin musayar ra'ayi da sa kaimi ga hadin gwiwa tsakanin Sin da Afrika.

Dadin dadawa, Mista Yang ya kara da cewa, Sin na fatan nacewa ga manufar zaman daidaici da shawarwari da juna, don gudanar da taron tare da kasashe 50 na Afirka, ta yadda za a mai da taron wani gaggarumin biki ne dake kara hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu da kuma habaka dangantakar dake tsakaninsu nan gaba. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China