in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin CNNC ya daddale yarjejeniyar kafa cibiyar nazari da kirkire-kirkire da Birtaniya
2015-10-20 21:04:33 cri
A yau Talata ne kamfanin samar da makamashin nukiliya na kasar Sin CNNC na kasar Sin ya bayyana cewa, ya daddale yarjejeniyar kafa cibiyar nazari da kirkire-kirkire da Birtaniya.

A yayin ziyarar da shugaban Sin Xi Jinping ke yi a kasar Birtaniya, a jiya Litinin bisa agogon wurin, an gudanar da taron shawarwari game da makamashi tsakanin Sin da Birtaniya na shekara-shekara karo na 4 a birnin London, inda bangarorin biyu suka rattaba hannu kan yarjejeniyar kafa cibiyar nazari da kirkire-kirkire ta Sin da Birtaniya.

An ba da labari cewa,tuni gwamnatin Burtaniya ta samar da kasafin kudi da wannan shiri, wanda zai zama abin koyi wajen yin nazari da hadin gwiwa a fannin fasahar nukiliya tsakanin Sin da kuma kasashe masu sukuni.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China