in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ziyarar shugaban kasar Sin a Birtaniya za ta karfafa hadin gwiwa a fannin tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen biyu
2015-10-15 14:04:01 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai ziyarar aiki a kasar Birtaniya daga ranar 19 zuwa 23 ga wannan wata.

A yayin da babban jami'in kwamitin cinikayya tsakanin kasashen Birtaniya da Sin Stephen Phillips ke zantawa da wakilinmu, ya ce, ziyarar shugaban kasar Sin a Birtaniyan za ta karfafa hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin kasashen biyu, kuma 'yan kasuwa da masu masana'antu za su ci gajiyar wannan dangantaka.

Stephen Phillips ya ce, a cikin 'yan shekarun nan, kamfanonin kasar Sin da dama sun zuba jari a Birtaniya, kuma Birtaniyar ta alkawarin bude kofa don yin maraba da masana'antun Sin da su zuba jari a kasar. Masana'antun Sin da dama ba ma kawai sun cimma nasara wajen zuba jari a Birtaniya ba, har ma sun shiga kasuwanni a kasashen Turai ta Birtaniya, ta yadda aka gaggauta aikin raya masana'antun Sin a kasashen waje.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China