in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ziyarar da shugaban kasar Sin zai kai Birtaniya tana da muhimmanci ga huldar kasashen biyu
2015-10-18 18:19:04 cri
Darektan darektocin kamfanin Standard Life na kasar Burtaniya, Gerry Grimsome a kwanan baya ya bayyana cewa, ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai kasar Burtaniya tana da muhimmanci, musamman ta fannin inganta huldar kasashen biyu da kuma harkokin zuba jari.

Mr.Grimsome ya sha kawo ziyara kasar Sin tun bayan shekarar 1992, wanda ya gane ma idonsa wasu muhimman al'amuran da suka shafi huldar kasashen biyu. Mr.Grimsome ya bayyana mamakinsa game da ci gaban ababen more rayuwa a kasar Sin. Ya ce, Burtaniya na da bukatar kyautata ababen more rayuwa a kasar, musamman ma tsarin hanyoyin mota da na jirgin kasa mai saurin gaske na zamani, don haka, kasashen biyu na da damar hada gwiwa da juna ta fannin raya manyan ababen more rayuwa. Ban da haka, kasar Sin na iya zuba jarinta a masana'antun samar da wutar lantarki masu amfani da makamashin nukiliya da hanyoyin dogo na zamani masu saurin gaske da kasuwannin gina gidaje da sauransu.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China