in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Afirka ta Kudu sun cimma matsayi kan yadda za a gudanar da taron kolin Johannesburg
2015-10-12 19:31:52 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a yayin taron maneman labarai da aka yi a yau Litinin cewa, kwanan baya, wakilin majalisar gudanarwar kasa ta Sin Yang Jiechi ya kai ziyarar aiki kasar Afirka ta Kudu a hukunce, inda ya tattauna da wakilan kasar Afirka ta Kudu kan yadda za a gudanar da taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka da za a yi a watan Disamba na bana, da kuma harkokin dake shafar ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai kasar Afirka ta Kudu da dai sauransu, ta yadda za a samu nasarar gudanar da taro da kuma ziyarar aiki da Xi Jinping zai kai a kasar.

Kasar Afirka ta Kudu na mai da hankali sosai kan ziyarar aiki da Yang Jiechi ya kai a kasar, inda bangarorin biyu suka cimma matsayi daya kan harkoki da dama, suna kuma ganin cewa, taron kolin da za a yi a birnin Johannesburg na da muhimmanci matuka wajen zurfafa hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, da kuma raya dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China