in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi ganawa tsakanin manyan jami'an kasar Sin da Amurka
2015-08-28 19:39:00 cri

Mambar majalisar gudanarwa ta kasar Sin Yang Jiechi ya gana da Susan Rice mai ba da taimako ga shugaban kasar Amurka kan harkokin tsaron kasar a ranar jumma'an nan 28 ga wata a nan birnin Beijing.

Yayin ganawar, Mista Yang ya ce, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai ziyarar aiki a Amurka a wata mai zuwa, wadda ke da babbar ma'ana ga bunkasuwar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da halin da duniya ke ciki. A cewarsa, ya kamata kasashen biyu sun kara hadin gwiwa a fannoni daban-daban saboda ganin sarkakiyar halin da dunya ke ciki.

A nata bangare, Madam Rice ta ce shugaban kasar Amurka Barack Obama ya nuna kyakkyawar fata ga ziyarar da shugaba Xi zai yi, sannan kuma yana jiran musanyar ra'ayi da shugaba Xi Jinping kan wasu manyan abubuwan duniya dake jawo hankalinsu. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China