in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan wasan Eritrea ya samu lambar yabo ta zinari cikin wasan Marathon
2015-08-22 13:30:12 cri

Yau Asabar 22 ga wata, dan wasan guje-guje da tsalle-tsalle na kasar Eritrea Ghirmay Ghebreslassie mai shekaru 19 ya samu lambar yabo ta zinari a wasan gudun dogon zango wato Marathon na maza, wato lambar yabo ta zinari ta farko da aka fidda cikin gasar fid da gwani ta duniya a wasan guje-guje da tsalle-tsalle na wannan karo da ake yi a birnin Beijing na kasar Sin.

Ghirmay Ghebreslassie ya kammala wasan Marathon din cikin awoyi 2 da mintoci 12 da dakika 28, sai kuma Yemane Tsegay wanda ya kai matsayi na takwas cikin gasar fid da gwani ta duniya ta wasan guje-guje da tsalle-tsalle da aka yi a shekarar 2013 ya samu lambar yabo ta azurfa cikin gasar na wannan karo, yayin da dan wasan kasar Uganda Munyo Solomon Mutai ya samu lambar yabo ta tagulla.

Haka kuma, cikin gasar na wannan karo, kasar Kenya wadda ta kasance gaba a fannin wasan guje-guje da tsalle-tsalle a kasashen duniya, ta aike da 'yan wasa guda uku domin halartar gasar a ciki hadda Dennis Kimetto wanda yake da matsayin bajintar duniya a hannunsa, amma Dennis Kimetto da wani dan wasan kasarsa ba su iya kammala gasar ba, dayan dan wasan kasar Kenya Paul Korir ya zama a matsayi na 22 cikin gasar da aka yi a yau. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China