Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ne ya kaddamar da bude gasar, tare da bayyana fara gudanar gasar wasannin motsa jikin a hukunce.
A nasa jawabi na bikin bude gasar, shugaban kwamitin shirya gasar wasannin motsa jikin Liu Peng, ya bayyana cewa cikin shekaru 54 da suka gabata, wato lokacin da aka kafa gudanar da wannan gasa, an yi ta kyautata ta, kuma ta kawo ci gaba mai tarin yawa ga aikace-aikacen wasannin motsa jiki a fadin kasar ta Sin.
Tawagogin 'yan wasannin motsa jiki guda 38 da suka kunshi 'yan wasa 9,770, daga sassan kasar Sin daban daban ne dai suka halarci gasar ta bana. (Maryam)