in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara gudanar da gasar kwallon tebur a Najeriya
2014-06-24 15:24:06 cri

Hukumar wasan kwallon tebur ta duniya ta baiwa Najeriya mai masaukin bakin gasar cin kofin Afrika na wasan kwallon tebur a shekarar 2014 a karo na farko, tuni dai aka fara gudanar da gasar a babban filin wasa na Teslim Balogun dake birnin Lagos na Najeriya. Za'a gudanar da gasar ne tsakanin ranar 23 zuwa 26 ga watan Yuni.

Ana sa rai cewa, Omar Assar, 'dan kasar Masar wanda ya taba samun kyautar zakara a gasar kwallon tebur ta Afrika, shi ma zai shiga gasar ta Lagos.

Sauran kasashe da za su taka rawa a gasar sun hada da Singapore, Masar, Rasha, Benin, Congo Brazzaville, da kuma jamhuriyar damokradiyya ta Congo, Kamaru, Ghana, Libya, Luxembourg, Morocco, Saliyo, Togo, Tunisia da kuma Najeriya, wacce ita ce mai masaukin gasar wasan.

Hukumar kwallon tebur ta duniya ta jera sunayen alkalan wasa har 36, domin shiga tsakani a wasan, wanda za'a yi kwanaki 4 ana yi.

Hukumar ta zabi alkalan wasan daga Najeriya, Ghana, Algeriya, Libya, Togo, Congo Brazzaville, da kuma Benin domin sa ido a wasan. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China