in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu cin hanci da rashawa ba za su iya tsere daga hukunci ba
2015-03-04 15:32:51 cri

 

Kakakin babban taro na 3 na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin na 12 Fu ying, ta ce kasar Sin na duba yiwuwar amfani da karin ka'idojin hukunta laifuffuka ta kasa da kasa, don nuna cikakken amfanin doka, da tsari na kasa da kasa, ta yadda za a sanya jami'ai masu cin hanci da rashawa fuskantar hukunci ko ina suka gudu.

Madam Fu ta ce, yanzu ana samun masu aikata laifin cin hanci da rashawa da yawa a kasar Sin, hakan na nufin ya dade ana samun matsala a wannan fanni, don haka dole ne a dauki matakai masu tsanani wajen yaki da cin hanci da rashawa. Haka kuma, a bangaren zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, ya kamata a karfafa tsarin yaki da cin hanci da rashawa, domin kafa wani yanayin da zai dakile yaduwar irin wadannan laifuffuka. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China