in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
CPPCC za ta tattauna batun zurfafa yin gyare-gyare
2015-03-03 20:27:50 cri

Majallisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin (CPPCC) ta bayyana kudurinta na kara kokarin zurfafa yin gyare-gyare a farkon makonni biyu masu muhimmanci a kalandar harkokin siyasar kasar Sin.

Shugaban majalisar Yu Zhengsheng wanda ya bayyana hakan yau lokacin da yake gabatar da rahoton aikin kwamitin hukumar a taronta na shekara-shekara ya ce, majalisar za ta mayar da hankali kan batutuwa guda hudu yayin take gudanar da ayyukanta.

Ya ce, wadannan muhimman batutuwa su ne batutuwan da shugaba Xi Jinping ya gabatar wadanda suka hada da gina al'umma mai annashuwa da wadata, tafiyar da harkokin mulkin kasa bisa dokoki, zurfafa yin gyare-gyare da kuma tafiyar da harkokin jam'iyya bisa doka.

Yu ya ce, shekarar ta 2015 shekara ce mai sarkakiya ga shirin zurfafa yin gyare-gyare, kuma shekara ce da aka kara zurfafa tafiyar da harkokin mulkin kasa bisa doka daga dukkan fannoni, kana shekara ce ta karshe ta kammala karo na 12 na ayyukan da aka tsara gudanarwa cikin shekaru biyar.

Don haka ya ce, kamata ya yi majalisar ta mayar da hankali kan shawarwarin da aka gabatar game da gyare-gyare da sauran ayyukanta da suka shafi ci gaban kasa a shekarar da ta gabata tare da tsara sabbin manufofin da ake son cimmawa a shekara 2015. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China