in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Sin na kiyaye 'yancin Musulmai na bin addininsu
2015-03-02 20:16:11 cri
Yau Litinin 2 ga wata, kakakin cikakken zama na shekara-shekara na majalissar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin karo na 12 Lv Xinhua ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin na mutunta da kuma kiyaye 'yancin Musulmai na bin addininsu yadda ya kamata.

A yau da yamma ne aka gudanar da taron manema labau kan cikakken zama na shekara-shekara, na majalissar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin karo 12 a nan birnin Beijing, inda Lv Xinhua ya ce, a farkon lokacin bude kofa ga waje, akwai masallatai kimanin dubu 2 a yanki mai cin gashin kansa na Uygur na jihar Xinjiang ta Sin, amma ya zuwa yanzu, ana da masallatai sama da dubu 20 a jihar, kana adadin ma'aikatan masallatan ya karu daga dubu 3 zuwa dubu 28. Kaza lika, tun farkon shekarar 2001 har zuwa yanzu, gaba daya gwamnatin jihar ta aike da mutane 47 zuwa wasu manyan jami'o'in Musulunci dake kasashen Masar, Pakistan da dai sauransu domin karo ilimi. Kana gaba daya an fitar da litattafai da mujallolin Musulunci na harshen Uygur kimanin miliyan 1 a jihar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China