Kakakin hukumar tsaron kasa ta Somaliya Mohammed Yusuf ya bayyana cewa, lamarin fashewar boma-boman da maharan suka aikata a sansanin rundunar sojan din ya tashi hankulan mazauna wurin sosai.
Wasu da lamarin ya faru gaban idanunsu sun bayyana cewa, fashewar boma-bomai ta lalata motoci guda hudu, da dukiyoyin jama'a.
Kungiyar tsattsauran ra'ayi ta "Somali Youth Party" ta sanar da daukar alhakin lamarin, domin mai da martani ga gwamnatin kasar da sojojin kasar Amurka, wadanda suka kai musu hari ta sama a kwanan baya, inda suka halaka shugaban kungiyar Ahmed Abdi Godane da kuma shugaban sashen leken asiri na kungiyar Abdi Shakour. (Maryam)