in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kame wani muhimmin garin dake gabar teku daga hannun Al-Shabaab a Somaliya
2014-10-06 17:22:26 cri
Rundunar dakarun wanzar da zaman lafia na kungiyar tarayyar Afrika dake Somalia, wato AMISOM sun kara kame garin Barawe dake gabar bakin ruwa, kamar dai yadda mazauna garin suka bayyana.

Gwamnatin Somalia da rundunar AMISOM sun ce garin ya fada hannun dakarun ba tare da fuskantar wani gagarumin gumuzu ba daga bangaren mayakan Al-shabaab, wadanda garin ya dade yana karkashin ikonsu.

Gidan Radiyo na Mogadishu ya ruwaito cewa, wani rukuni na dakarun wanzar da zaman lafiya da kuma na kasar ta Somalia sun kwace ikon mulkin garin daga hannun 'yan kungiyar ta Al-Shabaab, kuma a yanzu garin na hannun dakarun kiyaye zaman lafiyar.

Kame garin Barawe wata babbar nasara ce ga dakarun kiyaye zaman lafiya, wanda suka kaddamar da harin da motocin sulke tun watan Satumba da muradin tunkude 'yan tsageran Al-Shabaab daga wuraren da suka yi kaka gida. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China