in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mahukuntan Somaliya na daukar matakan ko-ta-kwana sakamakon kisan jagoran kungiyar Al-Shabaab
2014-09-07 15:56:45 cri
Mahukunta a kasar Somaliya sun ce yanzu haka an dauki matakan ko-ta-kwana, sakamakon bayanan sirri dake cewa kungiyar masu tsattsauran ra'ayin kishin Islama ta Al-Shabaab na shirin daukar fansar kisan shugabanta.

Wani harin da jirgi maras matuki na kasar Amurka ne dai ya hallaka jagoran kungiyar ta Al-Shabaab Ahmed Abdi Gonade a ranar Litinin din makon da ya gabata.

Bayan kusan mako guda da hakan ne kuma kungiyar ta tabbatar da rasuwar shugaban nata, tare da ayyana sunan Ahmed Omar Abu Ubeyda a matsayin sabon jagoranta.

Da yake karin haske game da matakan da gwamnatin kasar ke dauka domin dakile yunkuri da mayakan kungiyar za su yi na daukar fansa, ministan ma'aikatar tsaron kasar Khalif Ahmed Ereg, ya ce dakarun gwamnati za su ci gaba da sanya ido kwarai, musamman ganin yadda bayanan sirri ke nuna aniyar Al-Shabaab din na kaiwa gine-ginen hukuma hare-hare.

Daga nan sai ya yi kira ga al'ummar kasar da su taimaka wajen samar da duk wasu bayanan da za su taimakawa mahukunta wajen tabbatar da tsaro. Kaza lika Ereg ya bukaci mayakan kungiyar ta Al-Shabaab da su rungumi shirin lafiya cikin kwanaki 45, wanda gwamnatin Somaliyar ta tsara, duka dai da nufin kawo karshen tashe-tashen hankula da ake fuskanta a kasar. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China