in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dangantaka a tsakanin Somaliya da kasar Sin ba ta taba tsinkewa ba, in ji shugaban Somaliya
2014-10-12 16:27:10 cri
Shugban kasar Somaliya Hassan Cheikh Mohamoud ya nuna a ranar Asabar cewa huldar dangantaka tsakanin Somaliya da Sin na da dogon tarihi kuma ba ta taba tsinkewa ba tun a lokacin da aka maido da huldar diplomasiyya tsakanin kasashen biyu. A cikin wata hirar musammun tare da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Mogadiscio, shugaban Somaliya ya jaddada cewa dangantakar dake tsakanin kasarsa tare da kasar Sin tana nan har kullum, kuma matsalar tsaro ce ta hana jami'an diplomasiyyar kasar Sin zaman aiki a Somaliya.

Kasashen Sin da Somaliya na cin gajiyar dadadar dangantaka ta dogon tarihi. A yanzu haka, Somaliya da Sin, kasashe ne aminai, in ji mista Mohamoud jim kadan bayan ya dawo daga wani rangadin aiki a yankunan da aka karbe daga hannun kungiyar Shebab.

Gwamnatin Sin na samar da kayayyakin jin kai ga Somaliya tun lokacin faduwar gwamnatin tsakiya na Somaliya a shekarar 1991, in ji shugaba Mohamoud.

Ofishin jakadancin kasar Sin dake Somaliya ya rufe kofa fiye da shekaru ishirin, amma sake bude shi a ranar Lahadin da kuma nada sabon jakada za su taimakawa wajen karfafa huldar dangantaka tsakanin kasashen biyu, in ji shugaban Somaliya. Matsalar tsaro ta kyautatu a Somaliya, wannan ya kasance lokaci mai kyau domin maido da masu zuba jari na kasashen waje, har ma da kamfanonin kasar Sin, domin zuba jari a bangarori da dama na tattalin arziki in ji shugaba Mohamoud. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China