in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka mutu a sakamakon harin bom da aka kai ga babban birnin kasar Somaliya ya kai 20
2014-10-14 14:17:53 cri
Wani jami'in kasar Somaliya ya bayyana a ranar 13 ga wata cewa, an kai harin bom da aka dana a cikin wata mota a birnin Mogadishu a ranar 12 ga wata, wanda ya haddasa mutuwar mutane 20, yayin da mutane da dama suka ji rauni.

Wani jami'i a birnin mai suna Ahmed Nor ya bayyana cewa, an kara gano gawawwaki 6 a wurin da bam din ya fashe a ranar 13 ga wata, kafin wannan an gano gawawwaki 14, baki daya harin ya haddasa mutuwar mutane 20 a halin yanzu.

A ranar 13 ga wata, shugaban kasar Somaliya Hassan Sheikh Mohamud ya yi Allah wadai da wannan hari, inda ya zargi kungiyar Al-Shabaab da kai wannan hari.

Kana wakilan MDD da kungiyar AU dake kasar Somaliya su ma sun yi tir da harin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China