in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta samar wa wata makarantar a kasar Senegal kayayyakin karatu da na motsa jiki
2014-11-19 20:14:37 cri
Hadin gwiwar samar da ilmi yana daga cikin muhimman bangaren hadin gwiwa tsakanin Sin da Senegal, a kwanan baya ne, jakadan kasar Sin dake kasar Senegal ya sake samar wa wata makaranta daga karkarar kasar Senegal kayayyakin karatu da na motsa jiki.

A jiya Talata 18 ga wata ne, aka gudanar da bikin mika kayayyakin a makarantar sakandare ta Ndiar dake da nisan kilomita 60 daga babban birnin kasar, Dakar.

A shekarar 2009 ne aka kammala gina makarantar, wadda kasar Sin ta ba da taimako wajen gina ta, a halin yanzu, wannan makaranta na da dalibai guda 286 da kuma malamai guda 16.

A shekarar 2013, jakadan kasar Sin dake kasar Senegal ya taba samar wa makarantan na'urar kwanfuta, na'urorin nuna hotunan bidiyo da litattafai da sauran kayayyakin karatu da na motsa jiki. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China