in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata bangarorin biyu da rikicin Sudan ta Kudu ya shafa su warware sabanin da ke tsakaninsu ta hanyar zaman lafiya
2014-09-23 20:36:22 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a yau Talata 23 ga wata cewa, kasar Sin na tsayawa tsayin daka wajen nuna adalci kan batun kasar Sudan ta Kudu, ta kuma yi kira ga bangarorin biyu da rikicin kasar Sudan ta Kudu ya shafa da su warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar zaman lafiya, su kuma aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma yadda ya kamata.

Hua Chunying ta bayyana haka ne a yayin taron maneman labarai da aka saba yi a nan birnin Beijing, inda ta kuma yi bayani game da ziyarar da tawagar wakilan kasar Sudan ta Kudu suka kawo nan kasar Sin.

Bisa gayyatar da ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta yi masa, shugaban kwamitin harkokin wajen kungiyar adawa ta kasar Sudan ta Kudu Dhieu Mathok Diing Wol ya kawo ziyarar aiki a nan kasar Sin tare da wata tawagar kasar.

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi da mataimakinsa Zhang Ming sun gana da tawagar Sudan ta Kudu a jiya Litinin 22 ga wata, inda suka yi musayar ra'ayoyi kan yadda za a iya warware matsalar kasar Sudan ta Kudu ta hanyar zaman lafiya.

Hua Chunying ta kara da cewa, kasar Sin tana maraba da kungiyar raya gwamnatocin gabashin Afirka ta IGAD da ta taimaka wa kasar Sudan ta Kudu wajen warware matsalar kasar, don kiyaye zaman lafiya da zaman karko na kasar Sudan ta Kudu da na yankin baki daya, haka kuma, tana son taimakawa kasar wajen hanzarta warware matsalar dake fuskanta daga dukkan fannoni yadda ya kamta. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China