in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara taro karo na 6 na zagayen shawarwari na biyu kan Sudan ta Kudu
2014-09-23 10:05:01 cri

Zaman taro karo na shida na zagayen shawarwari na biyu kan zaman lafiya a Sudan ta Kudu ya bude a ranar Litinin a Bahir Dar, wani birnin kasar Habasha dake arewa maso yammacin kasar, in ji hukumar kasa da kasa kan cigaba ta IGAD, wata gamayyar shiyyar gabashin Afrika a cikin wata sanarwa.

Gyare-gyaren mulkin rikon kwarya, matakan kafa kundin tsarin mulki na din din din, gyare-gyaren da suka shafi tsaro cikin mulkin wucin gadi, kulawa da albarkatun tattalin arziki da na kudi, kana da batun shari'a da sasantawa game da rikon kwarya suna cikin manyan batutuwan da mahalarta taron za su mai da hankali kan su, in ji sanarwar. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China