in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An samu wasu dauke da cutar Ebola a gundumar Equateur ta DRC
2014-08-21 10:21:57 cri

An gano wasu mutanen dake dauke da cutar Ebola a gundumar Equateur dake arewa maso yammacin DRC-Congo, a cewar wata majiyar ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar da ba'a ambato sunanta ba a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Xinhua a ranar Laraba. A cewar wannan majiya, kusan mutane takwas ne ake zaton suna dauke da wannan cuta a gundumar. Ministan sadarwa na kasar kuma kakakin gwamnati, Lambert Mende ya karyata wannan labari a lokacin da kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya tuntube sa ta wayar tarho. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China