in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gano wasu mutane da aka zarge su da kamuwa da cutar Ebola a kasashen Jamus da Spaniya
2014-08-20 14:21:50 cri
A ranar 19 ga wata, an gano wata mata a birnin Berlin dake kasar Jamus da wani mutum a yankin Basque dake kasar Spaniya da ake zarge su da kamuwa da cutar Ebola, amma ya zuwa yanzu ba a tabbatar cewa ko sun kamu da cutar ko a'a ba.

A kwanakin baya ne, aka gano wasu mutane da aka zarge su da kamuwa da cutar ta Ebola a kasashen Jamus, Spaniya, Romania, Ruwanda, Senegal da sauran kasashe, amma aka janye zargin da ake musu daga baya. Ya zuwa yanzu, ban da kasashen Liberia, Saliyo, Guinea da Nijeriya, ba a gano wasu mutane da aka tabbatar sun kamu da cutar ta Ebola a wasu kasashe da yankuna ba.

Ban da wannan kuma, gwamnatin kasar Afirka ta Kudu ta bayyana a ranar 19 ga wata cewa, ana ci gaba da samun bunkasuwa a sha'anin yawon shakatawa a kasar, inda yawan masu yawon shakatawa daga kasashen waje bai ragu ba duk da matsalar cutar Ebola a Afirka. Ministan harkokin sadarwa na kasar Afirka ta Kudu Faith Muthambi ya bayar da wata sanarwa a wannan rana cewa, babu wani mutum da ya kamu da cutar Ebola a kasar ba. Kana ya ce, Ko da za a samun wanda ya kamu da cutar a kasar a wata rana, gwamnatin kasar na da imani da karfin tinkarar matsalar, bisa kyakkyawan tsarin sanya ido kan cututtuka da isassun na'urorin bada jinya da take da su. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China