in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zargin da yammacin kasashe suka yi wa Sin kan ayyukan zuba jari a Afirka ba su dace ba
2014-08-16 16:42:10 cri
Kwanan baya, wani shafin intanet na masanan diflomasiyya na kasar Japan ya fitar da wani sharhi, inda ya nuna cewa, sakamakon taimakon da kasar Sin ta baiwa kasashen Afirka ta hanyoyin yin hadin gwiwa da cimma moriyar juna, a halin yanzu, kasashen Afirka na mai da hankali sosai kan bunkasa harkokin kasuwancinsu, a maimakon dogaro kan taimakon da kasashen ketare suke ba su kamar da yadda suka taba yi a da. Shi ya sa, bai dace kasashen yammacin duniya su rika yi wa kasar Sin zargi dangane da harkokin zuba jari da take yi a kasashen Afirka.

Sharhin ya bayyana cewa, ba kawai harkokin hadin gwiwar da kasar Sin ta yi tare da kasashen Afirka suka tallafawa kasar Sin ba, har ma sun baiwa kasashen Afirka kayayyakin more rayuwa da suke bukata, da kuma tallafin kudi. Kana, a halin yanzu, kasar Sin ta kasance babbar abokiyar ciniki ta kasashen Afirka, ita ma abokiyar siyasa ta nahiyar Afirka, kwanan baya, kasar Sin ta kuma ba da muhimmin taimako ga yammacin kasashen Afirka wajen yaki da cutar Ebola.

Hakan ya sa, shugabannin kasashen Afirka suna mai da kasar Sin a matsayin abokiyarsu, a maimakon irin kasashen dake neman nuna karfin siyasa da nuna iko kan wasu kasashe da dama. Bugu da kari, sharhin ya bayyana cewa, ba shakka kasar Sin na ba da taimako ga bunkasuwar kasashen Afirka, da kuma daukaka matsayansu cikin harkokin kasa da kasa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China