in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin majalissun kasashen Sin da Nigeria sun yi ganawa
2014-05-12 21:28:02 cri

Shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar Sin Mr Zhang Dejiang ya gana da shugaban majalisar dattijan kasar Nigeria Mr David Mark a ranar litinin din nan 12 ga wata a babban dakin taron jama'ar kasar Sin dake nan birnin Beijing.

A lokacin ganawar, Mr Zhang ya ce, dangantakar dake tsakanin Sin da Nigeria ta zama abin koyi ga sauran kasashe saboda ganin ta shafi bangarori daban-daban bisa manyan tsare-tsare, ban da haka an samu ci gaba mai yakini a fannoni daban-daban. Kwanan baya kuma, Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya cimma nasarar a ziyararsa da ya kai Nigeria, inda bangarorin biyu sun daddale yarjeniyoyi da dama kan kara zuba jari da yin hadin kai, matakin da ya samar da wata makoma mai haske wajen zurfafa hadin gwiwa tsakaninsu.

A nasa bangare, Mr Mark ya ce, Sin sahihiyar abokiyar Nigeria ce, gwamnatin kasar Sin ta baiwa kasashen Afrika taimako a fannin raya tattalin arziki da al'ummominsu ciki hadda Nigeria, abin da zai kawo amfani sosai a cikin dogon lokaci. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China