in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kamala gasar koyon Sinanci mai taken"Gadar Sinanci" a birnin Lagos na Najeriya
2014-03-09 20:36:42 cri

An yi nasarar kammala gasar koyon Sinanci mai taken "Gadar Sinanci" ta shekarar 2014 da kwalejin koyon Sinanci ta Confucius na jami'ar Lagos dake kasar Nijeriya ya shirya a ran 7 ga watan Maris, wato dai-dai da bikin cika shekaru 10 da kafa wannan kwaleji.

A wannan rana, daliban da makarantun birnin Lagos guda 19 suka zaba sun halarci gasar, kuma wakilai sama da dari 5 daga bangaren da ya shafi al'adu, sha'anin kasuwanci na kasar Nijeriya, karamin ofishin jakadancin kasar Sin dake birnin Lagos, kungiyar 'yan kasuwa da kamfanoni na kasar Sin dake kasar Nijeriya sun kalli gasar da aka yi a jami'ar.

Bayan wannan gasa, mahalartar gasar sun nuna kaunarsu game da kasar Sin da kuma al'adunta, tare da nuna godiya ga kwalejin Confucius da ya shirya gasar, ta hanyar nuna abubuwan da suka koyo dangane da kasar Sin.

Shugabar kwalejin koyon Sinanci na Confucius na jami'ar Lagos Jiang Lirong ta bayyana cewa, kwalejin ya ciyar da shawarwari da hadin gwiwar al'adun kasar Sin da kasashen ketare gaba, ya kuma kara fahimtar jama'ar kasashen duniya game da Sinanci da al'adun kasar Sin, tare da ba da babbar gudumawa wajen karfafa dangantakar abokantaka dake tsakanin kasar Sin da kasashen ketare, da kuma bunkasuwar al'adun kasa da kasa bisa fannoni daban daban. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China