in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da jarrabawar Sinanci a kasar Nijeriya
2013-04-21 17:02:50 cri

A ranar 20 ga wata a sashen koyon adabi na jami'ar Lagos ta kasar Nijeriya, an gudanar da jarrabawar Sinanci mai lakabin HSK ta kwalejin koyon Sinanci wato Confucius.

An gudanar da jarrabawar Sinanci ta HSK a matakai biyu ne a jami'ar, inda dalibai 36 suka halarci jarrabawar. Bisa labarin da aka bayar, an ce, wannan ne karo na biyu da kwalejin koyon adabi ta jami'ar Lagos ta gudanar da jarrabawar HSK bayan da aka bude ta a shekarar 2012. Domin aikin koyar da Sinanci da ma'aunin koyon Sinanci na daliban kasar Nijeriya suka inganta, an gudanar da jarrabawar HSK a matakai biyu a wannan karo.

Daliban kasar Nijeriya suna begen shiga jarrabawar HSK tare da yin imani na cimma nasarar jarrabawar. Wani dalibi mai shiga jarrabawar HSK ta mataki na biyu Festus ya bayyana cewa, yana son koyon Sinanci sosai, shiga jarrabawar Sinanci zai sanya masa kaimin inganta kwazonsa na koyon Sinanci, tare da fatan cimma nasara a jarrabawar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China