in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bukaci Amurka ta mutunta yankin tsaron sararin samaniyar ta ADIZ
2013-12-05 15:27:36 cri
A ranar Alhamis din nan 5 ga wata, kasar Sin a cikin wata sanarwa da kakakin ma'aikatar harkokin wajen ta Hong Lei ya fitar, ta bukaci Amurka da ta mutunta yankin dake iyakokin tsaron sararin sama na tekun Gabashin kasar Sin cikin adalci.

Lokacin tattaunawa da mataimakin shugaban kasar Amurka da yake ziyara yanzu haka, kasar ta Sin ta jaddada daukan wannan matakin a tekun gabashin kasar ADIZ tana mai bayyana hakan da cewa yana bisa doka da kuma abin da aka saba gani a sauran kasashen duniya.

A cikin sanarwar, Mr. Hong ya bayyana cewa, shugabannin kasar Sin da mataimakin shugaban kasar Amurkan sun tattauna sosai kuma sun yi nazari mai zurfi a kan dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da sauran batutuwan da suka fi jawo hankalinsu a lokacin ziyarar Mr Biden. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China