in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a yi beli Hosni Mubarak amma ba za a maido da dukkiyarsa da aka karba ba
2013-08-22 14:37:39 cri

Kotun shigar da kara ta Alkahira ta yanke hukunci a ran 21 ga wata bisa agogon wuri, inda ta yarda da ba da belin tsohon shugaban kasar Hosni Mubarak.

Kotun ta yankewa Mubarak hukunci ne bisa zargin da aka yi masa na karbar kyautar kudin da ya kai miliyoyin kudin Masar daga kafar watsa labarai ta kasar.

Sakin shi da kotu ta yi ba ta bayyana cewa Mubarak ba shi da laifi ba , to amma bisa dokokin wuri, ba za a iya tsare da mutum sama da shekaru biyu ba, don haka, za a ba da belin shi. Kafar yada labaru ta kasar ta ba da labari cewa, ba za a yarda da Mubarak ya bar kasar Masar ko maido da dukkiyarsa ba, duk da cewar an sake shi.

An ce, an saki Hosni Mubarak makonni 7 bayan da sojojin kasar suka hambarar da gwamnatin Mohammed Morsi, abin da zai iya fusata jama'a daga wasu sassa, kana zai kawo cikas ga samun sulhu tsakanin al'umma. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China