in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kotun Masar ta yanke shawarar sake yin shari'a ga tsohon shugaban kasar Mubarak
2013-03-04 15:07:17 cri
A ranar 3 ga wata, kotun daukaka kara ta birnin Al'kahira na kasar Masar ta sanar da cewa, a ran 13 ga watan Afril za a sake gudanar da shari'a ga tsohon shugaban kasar Masar Hosni Mubarak, wanda aka tuhume da laifin murkushe masu zanga-zanga da makamai, a sa'i daya kuma, za a yi shari'ar 'ya'yansa guda 2, da tsohon ministan kula da harkokin cikin gida, da mataimakansa guda 6.

Cikin laifukan da ake tuhumar Mubarak da sauran mabiyansa, akwai laifin ba da umarni ga yin amfani da makamai don tarwatsa masu zanga-zanga, kana da sayar da iskar gas ga Isra'ila bisa farashi mai rahusa, tare da laifin cin hanci da rashawa. Ana dai sa ran gudanar da wannan shari'a ne a babbar kotun binciken manyan laifuffuka ta 10 dake birnin Al'kahira na kasar ta Masar.

A halin yanzu, Mubarak mai shekaru 84 na samun kulawar likitoci a wani asibitin soji na kasar. Idan dai za a iya tunawa a farkon shekarar 2011 ne, aka yi zanga-zangar kin jinin gwamnati a kasar ta Masar, lamarin da ya janyo hambarar da Mubarak daga mukaminsa. Bisa kididdigar da kafofin yada labaru suka yi, an ce, mutane kimanin 850 ne suka rasu cikin rikicin.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China