in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babbar kotun gudanarwa ta Masar ta yi watsi da karar da aka daukaka dangane da maido da aikin Mubarak
2013-04-03 10:51:09 cri
Kwanan baya, babbar kotun gudanarwa ta kasar Masar ta sanar da yin watsi da karar da wasu lauyoyi suka daukaka don maido da aikin tsohon shugaban kasar Muhammed Hosni Mubarak, watau ta yanke hukuncin cewa, Muhammed Mubarak ba zai iya komawa kan aikin mulkin kasar ba.

Bisa labarin da jaridar Al-Shorouk ta kasar Masar ta bayar kan shafinta na yanar gizo ta Internet a ran 1 ga wata da dare na agogon wurin, an ce, babbar kotun gudanarwa ta kasar Masar ta sanar da yin watsi da karar da aka daukaka dangane da maido da tsohon shugaban kasa Muhammed Hosni Mubarak kan mulki, inda kotun ta kuma kara da cewa, wannan shi ne hukunci na karshe, ba za a iya sake daukaka kara kan wannan batu ba.

Kafin wannan kara, wasu lauyoyi uku da wasu magoya bayan Mubarak sun taba daukaka kara a karamar kotun gudanarwa ta Masar don neman a maido da Mubarak kan aikinsa, amma karamar kotun ba ta yarda da wannan bukata ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China