in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasa Faransa ta ki baiwa tsohon mai aikin leken asiri na kasar Amurka Edward Snowden mafakar siyasa
2013-07-05 15:47:56 cri
Shafin Intanet na Vikileaks mai fallasa bayanan asiri ya ba da bayani cewa, tsohon mai leken asiri na kasar Amurka wanda ya fayyace asirin PRISM Edward Snowden ya riga ya roki kasashe har 21 da su ba shi mafakar siyasa.

A Jiya Alhamis 4 ga wata, ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Faransa ta ba da wata sanarwar kin yarda da rokon nasa.

Sanarwar ta ce, kamar yadda wasu sauran kasashe suka yi, ofishin jakadancin kasar Faransa dake kasar Rasha ta sami wata wasika daga wajen Edward Snowden domin neman samun mafakar siyasa a kasar. Amma, Faransa ta ki yarda saboda la'akari da shari'a da doka da kuma halin da Edward Snowden ke ciki.

Game da labarin da aka bayar na cewar Edward Snowden ya mikawa kasashe da dama ciki har da kasar Rasha wasikar rokon samun mafakar siyasa daga filin saukar jiragen sama na Sheremetyevo na kasar Rasha, mataimakin ministan harkokin waje na kasar Rasha Sergei Lavrov ya mai da martani a wannan rana cewa, har yanzu bai sami roko daga Snowden ba tukuna.

Har wa yau babu tabbaci kan wurin da Snowden zai tafi ba. An ce, a halin yanzu, yana yankin matafiyan da ke kan hanyar su ta wucewa na filin saukar jiragen sama na Sheremetyevo dake birnin Moscow na kasar Rasha. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China