in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka tana sa ran Rasha ta mika mata Snowden
2013-06-25 16:27:14 cri
Fadar 'White House' ta Amurka ta fada a ranar Litinin cewa, tana sa ran kasar Rasha za ta duba hanyar da ta dace ta tusa keyar mutumin da ya fallasa bayanan leken asirinta zuwa kasar ta Amurka.

Amurka dai na tuhumar Snowden mai shekaru 30 da laifin cin amanar kasa da satar bayanan gwamnati, sakamakon fallasa dimbim bayanan shirin Amurka na sa-ido kan bayanan wayoyi da na intanet.

Snowden wanda Amurka ke nema ruwa a jallo, ya bar Hong Kong a ranar Lahadi ne ta jirgin sama inda ya sauka a kasar Rasha, an kuma bayar da rahoton cewa, yana neman mafaka a kasar Equador.

Ko da yake wani jami'in kasar Rasha ya fada a ranar Litinin cewa, Amurka ba ta da iznin ta bukaci Rasha ta kama da kuma mika mata Snowden.

A cewar Vladimir Lukin mai rajin kare hakkin bil-adama a kasar Rasha, Snowden bai aikata wani laifi ba a kasar ta Rasha, sannan hukumomin Rasha ba su samu wata bukata daga kungiyar 'yan sanda ta kasa da kasa da ke kama masu laifi ba na neman a kama shi. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China