in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Amurka ta sanar da soke fasfon Snowden
2013-06-24 16:48:47 cri
Majalisar gudanarwa ta kasar Amurka ta bayar da sanarwa a daren jiya 23 ga wata, inda ta ce, an soke fasfon Snowden, tsohon 'dan kwangilar hukumar kula da bayanan sirrin tsaro ta Amurka NSA, wanda kasar Amurka ke zargi da tona asirin wasu bayanan sirrin tsaron kasar, da suka jibanci shirin leken asiri da gwamnatin ke gudanarwa ta yanar gizo, da kuma layukan wayoyin jama'a.

A cikin sanarwar, majalisar gudanarwar Amurka ta kira Snowden a matsayin mai laifin da ya gudu, ta kuma cewa, an soke fasfonsa ne kafin ya tashi daga HongKong zuwa Moscow. Bayan haka kuma, ta bayyana cewa, bai kamata a amince Snowden shiga ko wace kasa ba, saboda mummun laifin da gwamnatin kasar Amurka ke tuhumarsa da aikata wa a Jumma'a da ta gabata.

Da safiyar ranar Lahadin da ta wuce ne, jami'ai da 'yan majalisar dokokin kasar suka nuna mamaki da fushi game da batun Snowden yayin da suke ganawa da kafofin watsa labaru.

Wasu daga cikinsu sun yi tsamanin rahotannin da Snowden ya bayar sun kawo illa sosai ga kasar Amurka da aminanta, suna fatan gwamnatin Obama za ta cafke Snowden bisa dokokin da suka dace. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China