in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe da dama sun ki ba da taimako ga Edward Snowden wajen samun mafakar siyasa
2013-07-03 15:09:06 cri
Ya zuwa daren ranar 2 ga wata, bisa agogon Moscow, kasashe sama da 10 sun riga sun bayyana cewa ba za su samar da mafakar siyasa ga Edward Snowden ba wanda ya fallasa bayanan sirri na kasar Amurka, kana shugaban kasar Venezuela Nicolas Maduro Moros shi ma bai tafi da Edward Snowden ba, ko da akwai labarin cewa zai tafi tare da shi ta jirgin saman sa daga birnin Moscow.

Ran 2 ga wata, kungiyar WikiLeaks ta sanar da cewa, ta riga ta gabatar da sabbin takardun neman mafakar siyasa a madadin Snowden ga kasashe guda 19, da suka hada da kasashen Jamus, Venezuela, Rasha da dai sauransu. Ya kara da kasashen Ecuador, Iceland, wadanda aka riga aka mika musu takardun a baya. Gaba daya Wikileaks ta gabatar da takardun ga kasashe 21. Amma ya zuwa daren ranar 2 ga wata, kasashe sama da 10 sun riga sun bayyana cewa ba za su amsa rokon kungiyar ba. Bugu da kari, saboda bai iya amince da bukatar da shugaba Vladimir Putin ya fitar cewa kada ya dauki karin matakan da za su kawo wa kasar Amurka matsaloli ba, Edward Snowden ya riga ya yanke shawarar janye takardar neman mafakar siyasa da ya gabatar wa kasar Rasha.

Ban da wannan kuma, ran 2 ga wata da dare, bisa agogon Moscow, shugaban kasar Venezuela Nicolas Maduro Moros ya tashi daga birnin Moscow. Bisa labarin da aka samu, an ce, har zuwa yanzu, Edward Snowden na zauna a filin jiragen sama na kasar Rasha. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China