in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da wata gada a Nijeriya wadda kasar Sin ta ba da taimako wajen gina wa
2013-06-26 11:07:44 cri

An yi bikin kaddamar da wata gada a birnin Ibadan hedkwatar jihar Oyo dake kudu maso yammacin kasar a ran 25 ga wata, da reshen Nijeriya na kamfanin kula da ayyukan gine-gine na kasar Sin ya ba da taimako wajen gina wa.

Gwamnan jihar Abiola Adeyemi Ajimobi ya ce, wannan gadar ketare titi ta kasance ta farko a jihar da ta hada hanyoyi daban-daban da dama, wadda ta sake shaida karfin kamfanin bayan ya shiga aikin ceto bayan abkuwar ambaliyar ruwa a jihar. Ya ce, wannan aiki zai taimaka wajen sassauta halin da ake ciki a kudu maso yammacin kasar na rashin kyan hanya, da kuma ba da taimako wajen gaggauta bunkasuwar tattalin arziki da zaman al'umma a wannan yanki.

Manajan kamfanin Li Bing ya ce, kamfanin ya yi wannan aiki ne bisa iyakacin kokarinsa, wannan gada mai inganci ta nuna alamar kyan kamfanin a jihohi daban-daban da ke kudu maso yammacin kasar, har ma ta taka rawa wajen samar da guraben aikin yi da kyautata zaman rayuwar jama'ar wuri. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China