in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A Nijeriya kungiyar MEND ta dauki alhakin kaiwa wasu tankokin dakon mai hari
2013-06-16 16:07:46 cri
Kungiyar tsagerun Niger Delta dake kudancin Nijeriya ko MEND a takaice, ta ce, ita ce ke da alhakin dasa nakiyoyi a jikin wasu tankokin man fetur guda biyu, mallakar kamfanin sarrafa man fetur na kasar NNPC, dai dai lokacin da motocin ke barin harabar ginin kamfanin dake Abaji a Abuja, babban birnin tarayyar kasar.

Watan gajeriyar sanarwar da kakakin kungiyar Jomo Gbomo ya fitar bayan harin na ranar Asabar, ta bayyana kai harin a matsayin wani mataki na tirsasa gwamnatin kasar sakin daya daga jagororin kungiyar mai suna Henry Okah, wanda ba da jimawa ba aka yanke masa hukuncin dauri a kasar Afirka ta Kudu, bayan wata kotun kasar ta same shi da laifin aikata laifukan ta'addanci. Har ila yau cikin bukatun da kungiyar ta MEND ta bayyana, akwai saukar ministar man fetur ta tarayyar Nijeriyar Diezani Alison-Madueke daga mukaminta.

Gbomo ya ce, kungiyar ta MEND za ta ci gaba da kai makamantan wadannan hare-hare, har sai gwamnatin kasar ta biya dukkanin bukatun nasu. Tuni dai wani babban jami'in kamfanin man na NNPC ya tabbatar da aukuwar wannan lamari, ya kuma ce, ana nan ana ci gaba da bincike.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China