Shugaba Xi ya aike da sakon ta’aziyyar wadanda mahaukaciyar guguwar Rai ta halaka a Philippines
2021-12-21 20:47:19 CRI
A yau Talata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da sakon ta’aziyyar wadanda mahaukaciyar guguwar Rai ta halaka, ga takwaransa na kasar Philippines Rodrigo Duterte.
Shugaba Xi, ya ce ya kadu da jin labarin irin hasarar rayuka da dukiyoyi da guguwar mai hade da mamakon ruwan sama ta haddasa a makon jiya. Ya ce a madadin gwamnatin kasar Sin, da al’ummar kasar, da shi kan sa, yana mika sakon ta’aziyya ga ‘yan uwan wadanda wannan ibtila’i ya shafa, tare da jajantawa, da kuma fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata.
Shugaban na Sin, ya ce a shirye kasar Sin take ta taimakawa Philippines gwargwadon ikon ta. Ya ce yana da imanin yankin da wannan bala’i ya aukawa zai kai ga shawo kan lamarin, tare da sake ginuwa. (Saminu)
Labarai Masu Nasaba
- Shugaban Kasar Sin Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 40 Da Kafuwar Yankin Tattalin Arziki Na Musamman Na Xiamen
- Shugaba Xi ya jaddada muhimmancin karfafa dokokin jam’iyya domin kare jagoranci da gudanar da gwamnati cikin nasara
- Shugaba Xi Ya Gana Da Wakilan Al’umma Masu Ba Da Gudummawa Ga Wanzar Da Zaman Lafiya A Sin
- Xi da Thongloun sun shaida bude layin dogo tsakanin Sin da Laos tare