Sin na goyon bayan hanyar da kasar Rasha ta zaba
2021-09-20 20:41:25 CRI
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian, ya ce Sin za ta ci gaba da mara baya ga hanyar ci gaba da kasar Rasha ta zaba da kan ta, bayan da jam’iyyar kasar mai mulki ta lashe mafi rinjayen kuri’un da aka kada a zaben ‘yan majalisar dokoki.
Cikin wata sanarwa da ya fitar a Litinin din nan, Zhao Lijian ya ce zaben ‘yan majalissar dokokin Rasha, muhimmnin jigo ne a tsarin siyasar kasar, kuma sakamakon da aka fitar ya nuna alkiblar al’ummar kasar.
Kakakin ya kara da cewa, Sin za ta ci gaba da mara baya ga Rasha, ta yadda kasar za ta samu sabuwar nasara, karkashin jagorancin shugaba Vladimir Putin, har ta kai ga cimma burin ta na ci gaba da wadata. (Saminu)
Labarai Masu Nasaba
- Putin: Siyasantar Da Binciken Asalin COVID-19 Ba Madogara Ba Ce
- Kasar Sin tana fatan Amurka za ta waiwayi yanayin da ake ciki ta kuma guji aikata kuskuren da ta aikata a Afghanistan
- Sin Da Rasha Sun Amince Su Ci Gaba Da Aiwatar Da Yarjejeniyar Hadin Gwiwar Makwabata Da Abokanta
- Sin ta zargi Amurka da ficewa daga yarjejeniyar nan ta halasta shawagin jiragen saman kasashen juna