Kwamitin tsakiya na JKS da majalisar gudanarwar kasar sun taya tawagar kasar a gasar wasannin Olympics murna
2021-08-08 20:37:46 CRI
Kwamitin tsakiya na JKS da majalisar gudanarwar kasar Sin, sun aike da sakon taya murna ga tawagar kasar a gasar wasannin Olympics ta Tokyo.
Tawagar kasar Sin ta kammala dukkan gasanninta a Tokyo a yau Lahadi, inda ta lashe lambobin Zinare 38 da ta Azurfa 32 sai Tagulla 18. Tawagar ita ce ta zo ta biyu bayan Amurka, a yawan lambobin yabo. (Fa’iza Mustapha)
Labarai Masu Nasaba
- Shuagaban Namibia ya taya ‘yar wasan kasar murnar samun lambar Azurfa a wasannin Olympics
- Ese Brume ta samu lambar tagulla a wasan tsallen badake na mata
- Adadin lambobin Zinare da Sin ta samu a wasannin Olympics na Tokyo, ya dara wanda ta samu a wasannin Olympics na Rio
- An dakatar da ‘yar Nijeriya a wasannin Olympics na Tokyo saboda amfani da kayan kara kuzari