Shugaba Xi ya aike da sakon taya murnar bude baje kolin China-CEEC karo na biyu
2021-06-08 19:28:42 CRI
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da sakon taya murnar bude baje koli karo na biyu, na hadin gwiwar Sin da kasashen tsakiya da gabashin nahiyar Turai ko China-CEEC.
Cikin sakon da ya aike a Talatar nan, shugaba Xi ya yi fatan ganin dukkanin sassan dake da ruwa da tsaki a shirya baje kolin, sun yi amfani da damar dake cikin sa, wajen cin gajiyar hadin gwiwa da fadada cudanya.
An bude baje kolin na China-CEEC ne a birnin Ningbo dake lardin Zhejiang na gabashin kasar Sin. (Saminu)
Labarai Masu Nasaba
- Shugaba Xi Ya Fara Rangadi A Lardin Qinghai
- Xi Jinping: Karfafawa da inganta yin mu’amala da cudanyar bayanai a tsakanin Sin da kasashen ketare don nuna ainihin Sin
- Shugaban kasar Sin ya jaddada bukatar karfafa kimiyya da fasaha a muhimman matakai
- Shugaba Xi ya taya Bashar al-Assad murnar lashe zaben shugabancin Syria